Isa ga babban shafi
Afrika-Turai

Emmanuel Macron zai halarci taron shugabannin kasashen G5 Sahel

Shugaban Faransa Emmanuel Macron zai halarci taron shugabannin kasashen G5 Sahel dake yaki da Yan ta’adda wanda za’a gudanar da shi a Mauritania a makon gobe, a daidai lokacin da ake cigaba da samun karin hare hare daga Yan ta’addan.

Shugaban Faransa tareda Shugabannin kasashen G5 na Sahel  a garin Pau dake kasar Faransa
Shugaban Faransa tareda Shugabannin kasashen G5 na Sahel a garin Pau dake kasar Faransa Alvaro Barrientos/Pool via REUTERS
Talla

Rahotanni sun ce hare haren Yan ta’adda da kuma rikicin kabilanci sun zama ruwan dare a Yankin abinda ke kai ga rasa dimbin rayuka.

Tashe-tashen hankulla a tsakiyyar kasar Mali, dake fama da hare haren mayakan jihadi, rikici tsakanin kabilu da kuma wuce gona da irin da jami’án tsaro ke yi, sun yi sanadiyar mutuwar mutane 508 daga watan janairu zuwa yau.

Ana saran taron na ranar talata ya kunshi shugabanin kasashen Burkina Faso da Chadi da Mali da Mauritania da kuma Nijar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.