Sojojin Kamaru sun hallaka 'yan awaren da suka kashe dalibai 7
Gwamnatin Kamaru tace dakarun ta sun yi nasarar kashe 'Yan aware guda 5 cikin su harda wanda ya shugabanci 'Yan bindigar da suka kashe yaran makaranta guda 7 bara.
Wallafawa ranar:
Kakakin sojin kasar Cyrille Serge Atonfack Guemo ya tabbatar da kashe kwamandan Yan awaren a Balangui dake Kudu maso Yammacin kasar.
Jami’in yace sun kaddamar da hare hare ne domin kawar da Yan ta’addan da suka kai hari Kumba da kewayen sa, yayin da suka yi arangama da yan bindigar dake dauke da makamai.
Yan awaren Kamaru sun kaddakmar da munanan hare hare a yan shekarun da suka gabata abinda yayi sanadiyar rasa rayuka.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu