Isa ga babban shafi
Liberia

Kungiyoyi 15 a Liberia na son gwamnati ta kafa kotun hukunta laifukan yaki

Wasu kungiyoyin fararen hula guda 15 a Liberia, sun gabatar wa majalisar dokokin kasar bukatar ganin an kafa kotun da za ta hukunta masu aikata laifufukan yaki da cin zarafin bil’adama a kasar.

Shugaban kasar Liberia George Weah.
Shugaban kasar Liberia George Weah. AFP - LUDOVIC MARIN
Talla

Kungiyoyin sun ce lokaci ya yi da ya kamata a kafa wannan kotu a cikin kasar, shekaru 18 bayan yakin basasar da aka gwabza.

Muhawara kan kafa makamantan kotunan dai na ci gaba da fuskantar tarnaki ne tun daga lokacin mulkin shugaba Ellen Johnson Sirleaf da kuma bayan hawa mulkin George Weah a 2018.

Tun a shekarar 2009 wata hukuma ta musamman da kasar ta kafa don hukunta wadanda ke da hannu a aikata laifukan yakin shekaru 18 da suka gabata, ta bukaci samar da kotunan da nufin zartas da hukunci kan mutanen da kungiyoyi da kuma kamfanonin da suka rura wutar yakin basasar kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.