Isa ga babban shafi
Mali - Ta'addanci

Nakiya ta raunata dakarun Majalisar Dinkin Duniya 7 a Mali

Dakarun wanzar da zaman lafiya 7 sun ji rauni a tsakiyar Mali a ranar Juma’a, lokacin da motarsu ta taka nakiya da aka samar a gida, a cewar tawagar kiyaye zaman lafiya ta majalisar dinkin duniya.

Wani sojan Faransa na rundunar Barkhane yayin sintirin kakkabe 'yan ta'adda a garin Tin Hama dake kasar Mali, ranar 19 ga watan Oktoban 2017.
Wani sojan Faransa na rundunar Barkhane yayin sintirin kakkabe 'yan ta'adda a garin Tin Hama dake kasar Mali, ranar 19 ga watan Oktoban 2017. © REUTERS/Benoit Tessier/File Photo
Talla

Rundunar kiyaye zaman lafiyar ta Majalisar Dinkin Duhniya ta wallafa  a shafinta na Tweeter cewa nakiyar ta fashe a karkashin motar da dakarun ke ciki ne,  a yayin da suke kan hanyar zuwa Diallo, a tsakiyar yankin Mopti.

Ba a bayyana kasashen wadanda lamarin ya rutsa da su ba.

Tun daga shekarar 2012 ne ‘yan aware da masu ikirarin jihadi a arewacin Mali suka jefa kasar cikin tashin hankali da ya yi sanadin mutuwar dubban farar hula da mayaka, duk kuwa da taimakon kasa da kasa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.