Isa ga babban shafi
Mali

Yunkurin kashe shugaban Mali ba shi da nasaba da ta'addanci - rahoto

Masu bincikie a kasar Mali sun ce yunkurin daba wa shugaba mulkin sojin kasar, Kanar Assimi Goita wuka ba shi da nasaba da ta’addanci.

Shugaban gwamnatin mulkin sojin Mali, Kanar Assimi Goita.
Shugaban gwamnatin mulkin sojin Mali, Kanar Assimi Goita. MALIK KONATE AFP/File
Talla

An kai wa Goita hari ne yayin idin Sallah babba, a babban masallacin birnin Bamako a ranar Talata, sai dai maharin bai kai ga yi wa shugaban lahani ba, maimakon haka ya raunata daya daga cikin masu tsaronsa.

Goita wanda ya bayyana kafar talabijin kasar bayan aukuwar al’amarin ya  ce yana cikin koshin lafiya, inda ya yi watsi da harin a matsayin wani abin da bai taka kara ya karye ba.

An rantsar da Goita a matsayin shugaban Mali ne bayan da ya kifar da gwamnatin wucin gadi da ya ke aiki a cikinta  a matsayin mataimakin shugaba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.