Isa ga babban shafi
Sudan

Sojojin Sudan sun sallami jakadun wasu kasashe 6 daga kasar

Sojoji a Sudan sun bada sanarwar sallamar jakadun wasu kasashe 6, a dai-dai lokacin da suke kara zage damtse wajen tabbatar da tsaro da kuma shawo kan masu zanga-zangar nuna adawa da juyin mulki, wadda ta juye zuwa tarzoma a kasar.

 Abdel Fatah al Burhan, shugaban gwamnatin sojin Sudan
Abdel Fatah al Burhan, shugaban gwamnatin sojin Sudan . AFP
Talla

Matakin sallamar Jakadun na zuwa ne daidai lokacin kasashen duniya har ma da majaliar dinkin duniya ke kara matsa wa sojojin lamba da su gaggauta sakin Firayim Ministan kasar Abdallah Hamdok da suke tsare da shi.

Kasashen da sojojin suka sallami jakadun su daga kasar sun hadar da Amurka da China da Qatar da Faransa da Switzerland sai tarayyar Turai, abin da ake ganin ya faru ne saboda yadda suka yi tir da juyin mulkin.

Bayanai sun ce tuni sojoji suka fara amfani da karfin tuwo wajen murkushe masu zanga-zangar adawa da su, ta hanyar bude wuta, abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 7, kamar yadda hukumomin lafiya suka tabbatar, bayan mutane sama da dari da suka jikkata.

A yanzu dai zanga-zangar na daukar sabon salon juyewa zuwa tarzoma, ta yadda ta fantsama zuwa wasu manyan Birane irin su Omdurman mafi yawan al’umma a kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.