Isa ga babban shafi
Kamaru-Wasanni

Matsalar tsaro da corona sun addabi Kamaru gab da gasar cin kofin Afrika

Yayinda kasar Kamaru ta kammala dukkan shirye-shirye don fara wasannin gasar cin kofin Afrika da za a fara Lahadi mai zuwa, na tsawon wata daya, har yanzu akwai fargabar yadda za ta kasance  saboda matsalolin rashin tsaro a kasar.

Guda cikin filayen da za su karbi bakoncin wasannin gasar cin kofin Afrika a Kamaru.
Guda cikin filayen da za su karbi bakoncin wasannin gasar cin kofin Afrika a Kamaru. AFP - DANIEL BELOUMOU OLOMO
Talla

Wadanda za su bude wannan gasa a ranar lahadi mai zuwa dai akwai Kamaru, mai masaukin baki da za ta kara da  Burkina Faso.

Kasar ta Kamaru dai na fama da annobar  hare-haren ‘yan awaren yammaci,  ga kuma masu jihadi da karfin tsiya a gabashin kasar, al’amurran da ake fargaban kada ‘yan ta'addan su yi amfani da damar wasannin su kaddamar da hare-haren nasu.

Jami'an tsaro a kasar na cikin shirin ko ta kwana, bayanda aka sami wasu kungiyoyin ‘yan ta'addan na aikewa da sakonnin da ke barazana ga tarukan da za a yi.

Kungiyoyin wasan na rukunin F wato na shida, da suka hada da  Tunusia, Mali, Mauritania da Gambia ne dai suka sami sakonnina barazana ga ‘yan wasansu.

Wasannin da wadannan kasashen hudu za su yi ne a garin Limbe kuma suna motsa jiki ne a Buea masu hadarin gaske saboda rashin tsaro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.