Isa ga babban shafi
Zaben Gambia

Al'ummar Gambia na zaben 'yan majalisar dokoki

Al'ummar Gambia na kada kuri'ar zaben 'yan majalisar dokokin kasar a wannan Asabar, zaben da wasu ke ganin ka iya karfafawa shugaba Adama Barrow ikonsa bayan da ya sake lashe zabe a shekarar bara.

Wata rumfar zabe a kasar Gambia.
Wata rumfar zabe a kasar Gambia. © REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

‘Yan takarar shiga zauren majalisar dokokinkasar ta Gambia dai za su fafata ne akan kujeru 58 kan wa'adin shekaru biyar.

Sai dai daga cikin kujerun ‘yan Gambia za su zabi 53 uku ne, yayin da shugaba Barrow zai bayyana sunayen ragowar biyar da zai zaba, cikinsu har da shugaban majalisar.

Za a bude rumfunan zabe da karfe 8:00 na safe sannan a rufe da karfe 5 na yamma.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.