Isa ga babban shafi

Dakarun MNJTF sun halaka mayakan ISWAP 18 a Tafkin Chadi

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta kasa da kasa sun kashe wasu mayaka 18 da ake kyautata zaton na kungiyar ISWAP ne a yankin tafkin Chadi.

Wasu sojojin Nijar da ke rundunar kasa da kasa ta MNJTF yayin sintiri a Malam fatori dake Najeriya.
Wasu sojojin Nijar da ke rundunar kasa da kasa ta MNJTF yayin sintiri a Malam fatori dake Najeriya. AFP - PHILIPPE DESMAZES
Talla

Rundunar da a takaice ake kira da MNJTF ta kunshi sojoji daga Najeriya da Nijar da kuma Kamaru.

Bayanai sun ce dakarun hadin gwiwar sun halaka ‘yan ta’addan ne tun a ranar 3 ga watan nan na Afrilu bayan hare-haren da suka kaddamar kansu tsawon mako guda a yankuna da dama cikinsu har da Malam Fatori, Gashigar, da kumaTalata Ngam.

Baya ga kashe mayakan na ISWAP, sojojin sun lalata manyan bindigogi tare da kwato makamai da dama.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.