Burkina Faso zata dauki sabbin sojoji dubu 3 don yaki da ta'addanci
Gwamnatin Burkina Faso zata dauki karin sojoji dubu uku domin kara karfin sojojin kasar dake fama da hare-haren mayaka masu ikirarin jihadi, da akasari ke kaiwa ga rasa rayukan sojoji da fararen hula.
Wallafawa ranar:
Ministan Tsaron kasar, Janar Aimé Barthélémy Simporé yace, da farko an shirya daukar sojoji dubu biyu ne daga ranar 1 ga watan Yuni, da kuma Karin hafsoshi na musamman guda dubu daya, amma shirin zai soma daga ranakun 4 – 31 ga watan Mayu.
Kuma za’a zakulo zaratan ne daga jihohin kasar 13.
An yi kiyasanin Burkina Faso na da sojojin tsakanin dubu 15 zuwa 20, kuma akasarinsu sojojin kasa ne, da suka shafe shekaru bakwai suna fafatawa da mayaka masu ikirarin jihadi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu