Isa ga babban shafi

Yan adawar Chadi na zargin Gwamnati da kafar ungulu

Yan tawagar Chadi sun zargi gwamnatin kasar da jinkirin da ake samu wajen kulla yarjejeniya a taron zaman lafiya dake gudana a Doha.

Wasu sojojin kasar Chadi.
Wasu sojojin kasar Chadi. ASSOCIATED PRESS - Jerome Delay
Talla

Wannan taron na tattauna wa da ke gudana a Doha babban birnin Qatar an shirya shi ne ga kungiyoyi kusan 50 dake dauke da makamai a kasar Chadi, wanda aka shirya gudanar wa tun a ranar 27 ga watan fabarairu, aka kuma daga shi zuwa watan maris.

Tattaunawar da za’a warware matsalolin kasar da aka shirya yi a ranar 10 ga watan Mayu zata kunshi 'yan adawar siyasa da wadanda ke rike da makamai,  sannan a taron ne ya kamata a shirya managarcin tsari da za a samar da ingantaccen kundin tsarin mulkin kasar da kuma tsara sahihin zabe mai cike da adalci.

Taswirar kasar Chadi
Taswirar kasar Chadi © RFI

Kakakin gwamnatin Abderaman Koulamallah ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa, zarge-zarge ne ake musu da bai dace ba, domin suna da sha'awar ganin an kawo karshen tattaunawar da suka shirya a Qatar kafin ranar 10 ga watan Mayu domin 'yan siyasa da sojoji su kasance cikin tattaunawar da za a gudanar cikin adalci.

Taron sulhunta yan kasar Chadi a Doha
Taron sulhunta yan kasar Chadi a Doha AFP - KARIM JAAFAR

Indai ba a mance ba an dai nada Mahamat Idriss Deby Itno ne a matsayin shugaban majalisar soji ta rikon kwarya (CMT) da ta kunshi janar-janar 15, bayan sanarwar mutuwar mahaifinsa, Marshal Idriss Deby, a ranar 20 ga watan Afrilun shekara ta 2021, da aka kashe yayin fafatawa da yan tashin tashina.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.