Isa ga babban shafi

Sweden ta tasa keyar wani dan Rwanda domin amsa tuhuma kan kisan kare dangi

Hukumomin Kasar Sweden sun tasa keyar wani dan kasar Rwanda zuwa gida domin amsa tuhuma dangane da zargin da ake masa na hannu a kisan kare dangin da aka yi a kasar.

'Yan gudun hijirar Rwanda, a kan hanyar zuwa Byumba, bayan tserewa daga birnin Kigali, ranar 11 ga Mayu, 1994.
'Yan gudun hijirar Rwanda, a kan hanyar zuwa Byumba, bayan tserewa daga birnin Kigali, ranar 11 ga Mayu, 1994. AFP / Gérard Julien
Talla

Masu gabatar da kara a Kigali sun ce an mika musu Jean Paul Micomyiza yau laraba, yayin da suka godewa hukumomin Sweden akan taimaka musu da suka yi wajen yaki da kama karya.

An kama Micomyiza mai shekaru 50 a Sweden ne a watan Nuwambar shekarar 2020 sakamakon sammacin haka da Rwanda ta gabatar, yayin da akayi ta shari’a akan halarcin tasa keyar sa gida domin fuskantar tuhumar ko kuma akasin haka.

Ana tuhumar sa ne da hannu wajen neman Yan kabilar Tutsi inda suke nuna su domin hallaka su a shekarar 1994 lokacin yana matashi mai shekaru 22.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.