Isa ga babban shafi

An fara taron sassanta 'yan kasar Chadi a N'Djamena

A yau Asabar ake bude tattaunawar sassanta yan kasar Chadi mai cike da rudani tsakanin 'yan adawa, kungiyoyin farraren hula da shugabanin kungiyoyin yan tawaye da wakilan gwamnatin mulkin soja na. Taron da ake kyautata zaton zai taimaka  don shifuda sabon babe na shirya mika mulki da kuma ba da damar gudanar da zabuka a karkashin turbar dimokuradiyya. .

Taron sassanta yan kasar Chadi a Djamena
Taron sassanta yan kasar Chadi a Djamena © Christophe Petit Tesson/AFP
Talla

Mahamat Idriss Déby Itno, wanda ya hau kan karagar mulki a watan Afrilun 2021 bayan rasuwar mahaifinsa Idriss Deby, wanda ya mulki kasar na tsawon shekaru 30, ya yi alkawarin shirya wanan tattaunawa tare da kasanceewar dukkanin 'yan adawa don ba da damar dawo da mulki ga farar hula, a cikin watanni 18.

Shugaban gwamnatin sojin Chadi kenan, Idris Deby
Shugaban gwamnatin sojin Chadi kenan, Idris Deby © theguardian

Wakilai 1,400, mambobin kungiyoyin kwadago, jam'iyyun siyasa da na majalisar sojin kasar, za su yi taron na kwanaki 21, a N'Djamena babban birnin kasar, don tattauna batun sake fasalin hukumomi da sabon kundin tsarin mulkin kasar ta Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.