Isa ga babban shafi

'Yan sanda a Senegal sun fitar da jagoran 'yan adawa daga motarsa da karfi

Bayanai daga Senegal na cewa ‘yan sanda sun fasa gilasan babban madugun 'yan adawa Ousmane Sonko tare da tilasta masa fita daga motar sam jim kadan bayan bayyanar sa daga kotu. 

Jagoran 'yan adawan Senegal Ousmane Sonko.
Jagoran 'yan adawan Senegal Ousmane Sonko. © AFP - Seyllou
Talla

Hotunan bidiyo a shafukan sada zumunta da Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya gani sun nuna yadda 'yan sanda  suka fito dan siyasar mai shekaru 46 daga kujerar bayan motar, kafin daga bisani suka yi masa rakiya zuwa gidansa sai dai kakakin gwamnati ya musanta cewa an kama shi. 

Ana dai tuhumar Sonko da laifin cin mutuncin jama'a, da bata suna, zargin da ya biyo bayan Wanda aka ya yi wa ministan yawon bude ido na Senegal a wani taron manema labarai a karshen shekarar da ta gabata.  

Rahotanni sun ce jim kadan bayan fitowar daga kotun ya gaisa da magoya bayan sam dai-dai lokacin da ‘yan sanda suka fara harba hayaki mai as hawaye. 

Ousmane Sonko dai ya shiga bakin littafin gwamnatin kasar tun a shekarar 2011, lokacin da ya nuna adawar sa ga gwamnatin Macky Sall. 

Wannan sabuwar tuhuma dai na zuwa ne, bayan wadda aka yi massa ta fyade, laifin da idan aka tabbatar da shi zai shafe shekaru 10 a gidan yari. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.