Isa ga babban shafi

Harin ta'addanci ya yi sanadin mutuwar manoma 33 a Burkina Faso

A Burkina Faso, akalla mutane 33 ne suka mutu bayan da ‘yan bindiga suka bude wuta a kan wasu manoma a yankin yammacin kasar da ke fama da rikicin ‘yan ta’adda masu ikirarin jihadi, kamar yadda gwamnan yankin ya bayyana a jiya Asabar.

Sojojin Burkina Faso suna ta kokarin kawar da 'yan ta'adda masu ikirarin jihadi, amma suna gamuwa da cikas lokaci zuwa lokaci.
Sojojin Burkina Faso suna ta kokarin kawar da 'yan ta'adda masu ikirarin jihadi, amma suna gamuwa da cikas lokaci zuwa lokaci. © Issouf Sanogo, AFP
Talla

Gwamnan, Babo pierre Bassinga ya bayyana a wata sanarwa cewa harin ya auku ne a kauyen Youlou a yammacin Alhamis da misalin karfe biyar na yamma agogon GMT.

Majiyoyi masu karfi   daga yankin sun ce , ‘yan bindigar  da suka zo a kan babura, sun afka wa manoma fararen hula ne, wadanda ke noma a gefen kogi, inda suka yi musu harbin kan mai uwa da wabi.

A ranar Juma’a aka binne wadanda lamarin ya rutsa da su.

Rahotanni sun ce wasu mutane 3 sun samu munanan raunuka sakamakon harbin bindiga, kuma maharan sun kona wasu kadarori kafin su fara harbe-harbe.

Harin na ranar Alhamis din na zuwa ne ‘yan kwanaki bayan da aka tsinci gawar wani babban jami’i a yankin Boucle dun Mouhoun a cikin wani kungurmin daji.

Rikicin ta’addanci a Burkina Faso ya yi sanadin mutuwar mutane dubu 10 tare da daidaita miliyan 2.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.