Isa ga babban shafi

‘Yan sanda tara ne aka kashe a wani harin kwanton bauna a Somaliland

A Somaliland an kaiwa ‘yan sanda 9 harin kwanton bauna tare da kashe su bayan wata musayar wuta da aka yi,yankin da ya ayyana ‘yancin kai a Somaliya.

Birnin Hargeisa, babban birnin Somaliland
Birnin Hargeisa, babban birnin Somaliland AFP - EDUARDO SOTERAS
Talla

Lamarin ya faru ne tsakanin jami’an tsaro da ‘yan tawaye masu dauke da makamai a jiya  Juma'a a wani yanki mai tsaunuka mai tazarar kilomita 95 daga babban birnin yankin Hargeysa, in ji kwamandan 'yan sanda Mohamed Adan Saqadhi.

Taswirar yankin Somaliland
Taswirar yankin Somaliland © RFI

 'Yan bindigar "sun yi wa 'yan sanda 30 kwantan bauna kuma sun kashe tara", in ji Saqadhi, ya kara da cewa 'yan sanda 17 sun jikkata.

 A shekarar 1991 wani tsohon yanki na Birtaniya, Somaliland ya ayyana  kansa a matsayin yanki mai cikkaken ‘yancin kai daga Somaliya, yayin da wannan kasa ta fada cikin rudani da har yanzu ta kasa kawo karshen sa.

Wasu daga cikin mutanen Somalia
Wasu daga cikin mutanen Somalia AP - Jerome Delay

Tun a watan Yuli ne mahara suka dauki makamai domin nuna adawa da karin wa'adin da shugaban kasar Somaliland, Muse Bihi Abdi ya yi a watan Oktoban da ya gabata. Hukumar zaben Somaliland ta sanar a watan da ya gabata cewa za a gudanar da zabe zaben shugaban kasa a watan Nuwamba na shekarar 2024 , watanni 11 bayan zaben fidda gwani na jam'iyyar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.