Isa ga babban shafi

Hare-haren jiragen saman yaki ya kashe mutane 40 a wata kasuwar Sudan

Akalla mutabe 40 ne suka mutu, kana gwammai suka samu raunuka a yau Lahadi,  sakamakon wani hari da aka kai ta sama a wata kasuwa a  ke  babban birnin Sudan, Khartoum, a yayin   da  yakin da ake a kasar ke daf da cika watanni 5.

Tun a watan Afrilu ne yaki ya barke a Sudan, tsakanin sojoji da rundunar kai daukin gaggawa ta RSF.
Tun a watan Afrilu ne yaki ya barke a Sudan, tsakanin sojoji da rundunar kai daukin gaggawa ta RSF. © AP
Talla

Wannan adadi na nuni da cewa harin shine guda 1 mafi muni da aka taba kaiwa tun da wannan yaki ya barke a watan Afrilu, sakamakon rashin jituwa tsakanin sshugabann rundunar sojin kasar, Janar Abdel Fattah al-Burhan da tsohon mataimakinsa mai jagorantar rundunar kai daukin gaggawa ta  RSF,  Mohamed Hamdan Daglo.

Rahotanni sun ce da misalin karfe 5 da rabi agogon GMT jirgin saman yaki na sojin Sudan ya yi luguden wuta a yankin kasuwa  Quoro.

Wata  kungiya da ke bada gudummawa    ga fararen hula a yaayin wannan yaki ta ce adadin mamata na iya  karuwa kowane lokaci daga yaanzu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.