Isa ga babban shafi

An kaddamar da yakin neman zaben shugabancin Jamhuriyar Demokradiyar Congo

An kaddamar da yakin neman zabe a Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo har na tsawon wata guda ranar Lahadi, kafin babban zaben da ke tafe cikin watan Disamba.

Shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo Felix A. Tshisekedi, yayin yayin neman zabe. 19/11/23
Shugaban kasar Jamhuriyar Demokradiyar Congo Felix A. Tshisekedi, yayin yayin neman zabe. 19/11/23 © Felix A. Tshisekedi (Parody)
Talla

'Yan takara 26 cikin har da shugaba mai ci Felix Tshisekedi ke fafatawa a neman shugabancin kasar, daidai loakcin da gabashin kasar ke fama da hare-haren kungiyoyi masu dauke da makamai. 

Kimanin masu kada kuri’a miliyan 44 ne suka yi rajista, daga cikin al’ummar kasar kusan miliyan 100, da za su zabi shugaban kasa a ranar 20 ga watan Disamba. 

Za kuma su zabi tsakanin ‘yan majalisar dokoki da shugabannin kananan hukumomi a kasar mai dumbin albarkatun kasa, amma rikece-rike da cin hanci da rashawa ya yi mata katutu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.