Isa ga babban shafi
KWALON KAFA

CAF, ta nada El Hadji Diouf, Asamoah Gyan, Ahmed Hassan da Augustine 'Jay-Jay' Okocha a matsayin jakadunta

Shahararun zakarun tarihin kwallon kafar nahiyar Afrika irinsu El Hadji Diouf, Asamoah Gyan, Ahmed Hassan da  Augustine 'Jay-Jay' Okocha sun kasance  sunayen  farko da aka nada jakadun hukumar  kwallon kafar nahiyar Afrika Caf a karkashjin wani sabon shirin da aka kirkiro.Rawar da za su taka, ta ta’allaka ne wajen kokarin zaburar da ci gaba ga  hukumar CAF, da kuma inganta yanayin kwallon nahiyar Afrika. 

tsohon dan kwallon kafar Najeriya Jay-Jay Okocha, a daura da  tsohin yankwallon  Maroko Houssine Kharja,
tsohon dan kwallon kafar Najeriya Jay-Jay Okocha, a daura da tsohin yankwallon Maroko Houssine Kharja, AP
Talla

Haka kuma za su taka muhimmiyar rawa a cikin wasu ayuka masu muhimmanci  da suka hada da shirya kwambalar, tare  da tafiyar da sabon shirin  ayukan jinkai, harakokin kasuwanci da kuma na kyautata jin dadin rayuwar al’umma da dai sauransu.

Tsarin da aka bi wajen zaben wadannan kwararu a fannin kwallon kafar da suka bar tarihi mai armashi, da kuma suka kasance mutane ne da aka sani cikin jama ;a sosai, bai takaita kawai daga kwarewar da suka samu a fannin kwallon kafar kwararu kawai ba, ya hada ne da kasuwanci da kuma irin matsayin da suke da shi ne a cikin al’umma.

Diouf, sau biyu yana sabe gambin dan wasa mafi kwarewa na hukuma CAF Awards, na ci gaba da tsayawa a cikin kwakwale sakamakon namijin kokarin da ya yi a  kungiyar  Lions de la Teranga du Sénégal. Tare da kyakywan tarihin kurciyar da ya bari a 2000 a kwata final na gasar cin kofin nahiyar Afrika na shekara ta  2002 tare da buga wasan kwata final na gasar cin kofunan duniya a kasashen  Coréa ta kudu da Japon.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.