Gobara ta kashe mutane da lalata motoci da kadarori na kasuwanci a Nairobi
Akalla mutane uku ne suka mutu yayin da wasu fiye da 270 suka jikkata sakamakon wata gobara da ta tashi a wata babbar mota dauke da iskar gas a babban birnin kasar Kenya.
Wallafawa ranar:
Fashewar a cewar mai magana da yawun gwamnati Isaac Maigua Mwaura, gobarar ta kara lalata motoci da dama da kuma kadarori na kasuwanci. “Abin takaici, gidajen zama a unguwar suma sun kone kurmus.
Mataimakin Sufeto Janar na ‘yan sandan Najeriya Douglas Kanja ya shaida wa manema labarai cewa akalla mutane uku ne suka mutu sannan 271 aka kwantar da su asibitoci daban-daban a birnin Nairobi. Gobarar ta tashi ne a cikin daren jiya Alhamis a unguwar Embakasi a kudu maso gabashin babban birnin kasar. Hotunan da kafafen yada labaran kasar suka yada sun nuna wutar ta kama gidaje da dama. Felix Kirwa, wani direban tasi ne, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa AFP cewa ya dawo gida ne lokacin da ya ji karar fashewar wasu abubuwa guda biyu da ya sa gidansa ya girgiza tare da farfasa tagar.
Wannan dai bas hi ne karo na farko da aka ta ba samun irin wannan gobara, ko a shekarar 2018, wata gobara da ta tashi a kasuwar Gikomba ta Nairobi ta kashe mutane 15 tare da jikkata akalla 70. Tara daga cikin wadanda suka mutu suna cikin wani gida ne da ke kusa da kasuwar yayin da wasu shida,ciki har da yara hudu suka mutu sakamakon raunukan da suka samu a asibiti.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu