Isa ga babban shafi
Isra'ila-Palasdinawa

Hamas ta mikawa Isra’ila shalit ta hannun hukumomin Masar

Kungiyar Hamas ta mikawa dakarun Isra’ila Shalit ta hannun hukumomin Masar masu shiga tsakanin yarjejeniyar musayar fursunoni tsakanin Isra’ila da palesdinu.Tuni aka saki Palasdinawa 477 da Isra’ila ke tsare da su a gidan yari. Sama da Fursunoni 1,000 ne kuma ake sa ran Isra’ila zata saki bayan mika mata Gilad Shalit.A shekarar 2006 ne kungiyar Hamas ta kama Gilad Shalit bayan kaddamar da yaki.Tun da safiyar yau Talata ne Hamas ta dauki Gilad Shalit zuwa Rafah yankin da ke tsakanin Gaza da Masar domin mika shi ga wakilan Isra’ila.A watan gobe ne Isra’ila zata saki sauran fursononin Palesdinu Bayan sakin wasu daga cikinsu. 

Hoton Sojan Isra'ila Gilad Shalit.
Hoton Sojan Isra'ila Gilad Shalit. ©Reuters.
Talla

02:11

Dr Sadiq Alkafawi a Jami’ar Ahmadu Bello Zariya Najeriya

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.