Isa ga babban shafi
Syria

Ana ci gaba da rikici a Syria bayan ziyarar masu sa ido

Tawagar Kungiyar kasashen Labarawa na ci gaba da sa ido a sassan kasar Syria, yayin da ake cigaba da tashin hankali inda ‘Yan rajin kare Hakkin Bil adama ke tabbatar da mutuwar mutane 10 sanadiyar dauki ba dadi tsakanin Masu zanga-zanga da Jami’an tsaro.

Wani Hoton bidiyo ta Youtube  da ke nuna wakilan kasashen Larabawa a kasar Syria inda suke aikin sa ido a cikin kasar
Wani Hoton bidiyo ta Youtube da ke nuna wakilan kasashen Larabawa a kasar Syria inda suke aikin sa ido a cikin kasar AFP/Youtube
Talla

Amma shugaban tawagar Larabawan ya musanta rahotannin da kungiyoyin ke yadawa, inda yake cewa, shi ya zuwa yanzu bai ga wani abu mai tada hankali ba.

A bangare daya kuma, shugaba Bashar al Assad ya saki mutane 755 da aka kama a lokacin tashe tashen hankulan.

Waikilan kungiyar zasu kai ziyara birnin Hama da yankin arewa masu gabacin Idib da kudancin birnin Deraa inda aka fara gudanar da zanga-zangar a kasar.

‘Yan rajin kare hakkin Bil’adama sun ce akalla mutane 40 sun mutu cikin kwanaki biyu da fara ziyarar wakilan kungiyar Larabawa a cikin kasar.

Kungiyar kare hakkin bil’adata mai sa ido a kasar Syria tace an kashe wasu Soji hudu da suka canza sheka a birnin Deraa da kuma fararen hula da aka kashe a gundumar Amr a birnin Homs da kuma yankin Hama da Aleppo.

Shugaban wakilan kungiyar Janar Mustafa al-Dabi, dan kasar Sudan ya shaidawa kamfanin Dillacin Labaran Reuters cewa al’amurra sun fara sauyawa a kasar amma kuma basu ga wani abun tashin hankali ba kawo yanzu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.