Fada ya rincabe cikin kasar Syria
Rahotanni daga birnin Damascus na kasar Syria na cewa ana ta barin wuta da hargitsi a tsawon yau Littini, tsakanin dakarun kasar da masu kyamar Gwamnatin Shugaba Bashar al-Assad, da kuma masu biyayyawa gwamnati
Wallafawa ranar:
A yau dinne kuma ayarin musamman da MDD da kungiyar kasashen Larabawa ta nada domin sasanta rikicin kasar, karkashin jagorancin Kofi Annan, ke sauka a kasar domin ci gaba da aikin nasu.
Kazamin fadan na a daidai yammacin birnin Damascus ne ya fi kamari, kuma ana ganin munin fadan na yau yafi na kowace rana a tsawon shekara daya da aka yi ana fafatawa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu