Isa ga babban shafi
Syria

Syria : Brahimi ya yi murabus

Bayan shafe tsawon lokaci yana kokarin kawo karshen yakin basasan kasar Syria ba tare da nasara ba, mai shiga tsakani na Majalisar Dinkin Duniya da kungiyar Hadin kan kasashen Larabawa Lakhdar Brahimi ya bayar da sanarwar yin murabus.

Lakhdar Brahimi, manzon Majalisar Dinkin Duniya kan rikicin Syria
Lakhdar Brahimi, manzon Majalisar Dinkin Duniya kan rikicin Syria REUTERS/Denis Balibouse
Talla

Brahimi zai ajiye aikin shiga tsakanin rikicin Syria daga ranar 31 ga wannan watan na Mayu

Brahimi Dan Asalin kasar Algeria, mai shekaru 80 a duniya, ya sami nasarar kawo bangaroron gwamnatin Bashar al-Assad, da ‘yan tawayen Syria su shiga tattaunawar zaman lafiyan da aka shirya a birnin Genevan kasar Switzerland har sau 2, a bana.

Sai dai wannan karon, kokarin na Brahimi ya gagara kawo karshen yakin basasar Syria, da ya lakume rayukan fiye da mutane dubu 150, wasu miliyoyi kuma suka rasa gidajen su cikin shekaru uku.

Kokarin sasanta rikicin na Syria ya sake samun koma baya, sakamakon takun saka tsakanin Amurka da Rasha, kasashe biyu da ke tallafawa Brahimi, da kuma yanzu ke cacar baki kan makomar kasar Ukraine.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.