Isra’ila zata ci gaba da kare muradun ta
Israila tayi alkawarin cewar ba zata bari Yahudawa masu tsatsauran ra’ayi su shiga Masallacin Al Aqsa ba, abinda ya haifar da tashin hankali a Birnin Kudus yanzu haka.Fira Ministan Benjamin Netanyahu ya bayyana haka a hirar da suka yi da Sarki Abdallah na Jordan ta waya kan tahsin hankalin da ake samu .
Wallafawa ranar:
Isra’ila na ci gaba da yi kira zuwa musulamai yan Falesdinu na gani sun kaucewa tada kaya baya a harabar shiga masallacin Al Aqsa.
Yayi da a dai wajen yahudawa masu tsatsauran ra’ayi ke cigaba da nanata cewa sune ya dace sun malaki wanan muhimi wuri duk da kokarin jami’an tsaro na hanu su shiga harabar masallacin.
Rahotani daga yankin na nuni da cewa sama da matasa yahudawa 150 ne yanzu haka ke kokarin kilace hanyoyin zuwa masalacin Al Aqsa daga garin Tel Aviv.
Gwamnatin Israila domin kaucewa duk wata barazana da zata sake tsuduma yankin cikin wani sabon rikici ta aiwatar da doka ta musaman,wace ta haramtawa duk wani mutun dan kasa da shekaru 35 shiga wanan masallaci a yau juma’a domin gudanar da ibadar sa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu