Isa ga babban shafi
Nepal

EU ta ce akwai 'yan kasashenta da suka bata bayan girgizar kasar Nepal

Kungiyar Kasashen Turai ta ce har yanzu akwai wasu ‘yan kasashenta dubu 1, da ba su ji duriyar su ba tun bayan aukuwar mummunar Girgizar kasa a Nepal ya kashe dubban mutane  

Wani Kauye da girgizar Kasar Nepal ta dai-dai ta
Wani Kauye da girgizar Kasar Nepal ta dai-dai ta REUTERS/Athit Perawongmetha
Talla

Jakadan Kungiyar Kasahen Turai a Nepal, Rensje Teerink ya ce, akwai yan kasashensu da dama dake zuwa tsaunin Everest kusa da inda Girgizar kasar mai girman maki 7.8 ta shafa a Kathmandu babban birnin kasar

Rensje ya ce, har yanzu basu da labari dangane da halin da ‘yan kasashensu a yankin ke ciki, sai dai ana zatan watakila wasun su na yankin da wayar sadarwa bata kai wa.

Rahotannin na cewa, Mutane da dama mummunar girgizar kasar ta shafa na cewa, ba su samu komai na taimako ba, kusan mako guda bayan aukuwar bala'in.

Gwamnatin Nepal na cigaba da yin kira ga gwamnatocin kasashen waje da su kara aikawa da jirage masu saukar ungulu domin kai kayan agaji zuwa wurare masu nisa dake yankunan tsaunuka.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.