Isa ga babban shafi
Nepal

Akwai yiwuwar barkewar cututtuka a Nepal

Bayan afkuwar bala’in girgizan Kasa a Nepal, kwararru sun bayyana cewa, akwai yiwuwar barkewar cututtuka, sakamkon  ruwan masai daya karade wurare da kuma yadda gawarwaki da ke ci gaba da doyi, yayin da dubban mutane ke kwanciya a sararin Allah.

Mutane da ke kokarin tserewa a Katmandou
Mutane da ke kokarin tserewa a Katmandou
Talla

lamarin dai ya tada hankulan kwararru, wanda ke dari-darin yiwuwar barkewar cututtuka tsakanin al-ummar kasar

An taba samu irin wannan lamarin a kasar Haiti a lokacin data gamu da bala’in girgizan kasa a shekara ta 2010, inda cutar kwalara ta yadu tsakanin al-umma saboda gurbacewar ruwan sha bayan aukuwar girgizan kasar.

Patrick Fuller, babban jami’i ne a hukumar bada agajin gaggauwa ta Red Cross, ya shaidawa kamfanin dillacin labaran faransa cewa, akwai yiwuwar samun cututtuka kamar amai da gudawa tsakani al-umma dake shan gurbatattacen ruwa a yanzu

Kawo yanzu dai, dubban jama’a ne suka shafe tsawon kwanaki biyar a sararin Allah a Kathmandu babban birnin kasar Nepal, yayin da kuma suka rasa tsaftataccen ruwan sha kuma suke bahaya a filin da su ke.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.