Zazzabin Ciwon sauro na hallaka mutane a India
India ta umarci samar da Karin gadaje dubu daya a asibitin birnin Delhi sakamakon sabuwar cutar zazzabin ciwon sauro, mafi muni da ya barke a kasar karon farko a shekaru biyar
Wallafawa ranar:
Gwamnatin kasar ta bayyana furgabanta matuka bayan mutuwar wasu Iyayen wani yaro mai shekaru 7, da ya mutu sakamakon zazzabin cizon sauro da ya barke a kasar.
Bayan mutuwar wannan yaro ne dai mahaifinsa da mahaifiyarsa suka kashe kan su saboda bakin cikin abinda ya same dan su.
Sama da mutane 1,714 ne zazzabin ya durkusar a wannan shekarar a kasar, musamman a ‘yan makonin nan.
A cewar Darakatan Ma’aikatar Kiwon Lafiya birnin Delhi YK Mann akwai yiwuwar sake samun yaduwar zazzabin anan gaba lura da halin da ake ciki a yanzu.
Kawo yanzu dai mutane 8 zazzabin ya hallaka
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu