Isa ga babban shafi
Bangladesh

An rataye 'yan adawa biyu a kasar Bangladesh

Hukumomi a kasar Bangladesh, a yau lahadi sun zartas da hukuncin kisa ta hanyar ratayewa a kan wasu ‘yan adawa biyu na kasar wadanda aka sama da aikata miyagun laifufuka a lokacin da kasar ke gwagwarmayar ballewa daga Pakistan a shekarun 1970.

Masu zanga-zanga a birnin Dhaka
Masu zanga-zanga a birnin Dhaka AFP PHOTO/ Munir uz ZAMAN
Talla

Magoya bayan jam’iyya mai mulki a kasar sun gudanar da bukukuwa na farin ciki a game da rataye Ali Ahsan Mohammad Mujahid da kuma Salahuddin Quader Chowdury, lamarin da ya yi matukar tunzara magoya bayan ‘yan adawa.

Yanzu haka dai an baza dimbin jami’an tsaro a birnin Dhaka fadar gwmanatin kasar domin kasancewa a cikin shirin ko-ta-kwana.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.