Isa ga babban shafi
Syria

Amnesty ta zargi Rasha da kashe fararen hula a Syria

Kungiyar Amnesty International ta zargi Rasha da kashe daruruwan fararen hula a hare haren saman da ta ke kai wa a Syria, inda ta ce hakan na iya zama laifukan yaki.

Jiragen yakin Rasha na kaddamar da hare haren sama a Syria
Jiragen yakin Rasha na kaddamar da hare haren sama a Syria REUTERS/Ministry of Defence of the Russian Federation/Handout vi
Talla

Philip Luther, daraktan kungiyar da ke kula da yankin Gabas Ta Tsakiya da Arewacin Afrika ya ce, wasu hare haren ana kai su ne kawai kan fararen hula ko kuma gidajen jama’a da asibitoci.

Kungiyar ta ce binciken da ta yi ya nuna cewa, a cikin watanni uku da fara kai hare haren biranen Homs da Idlib da Aleppo, Rasha ta hallaka fararen hula sama da 200

Rasha dai ta ce tana kaddamar da farmaki ne kan 'yan ta'adda.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.