Isa ga babban shafi
Syria

ISIS ta kashe mutane fiye da 100 a Syria

Akalla mutane 101 ne suka rasa rayukansu sakamakon munanan hare haren da kungiyar ISIS ta kaddamar a sansanonin sojojin Syria a wannan Litinin.

Kungiyar ISIS ta dauki alhakin kashe mutane 101 a Syria
Kungiyar ISIS ta dauki alhakin kashe mutane 101 a Syria SANA/Handout via Reuters
Talla

Kungiyar da ke sa ido kan hakkin dan Adam a Syria ta ce, mayakan sun kai harin farko  a birnn Jableh, inda nan take suka kashe mutane 53 yayin da hari na biyu da aka kai a birnin Tartus ya lakume rayuka 48.

Rahotanni sun ce, wannan dai, shi ne farmaki mafi muni da aka kai a biranen tun bayan da Syria ta fada cikin rikici a shekara ta 2011.

Jim kadan da aukuwar lamarin ne, kungiyar ISIS mai da’awar jihadi ta sanar da daukan alhakin hare haren na kunar bakin wake.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.