china
Guguwa ta kashe mutane 78 a China
Mutane 78 aka tabbatar da mutuwarsu yayin da wasu kusan 500 suka samu raunuka sakamakon wata guguwa mai dauke da ruwan sama da ta mamaye yankin Jiangsu da ke gabashin kasar China.
Wallafawa ranar:
Talla
Kamfanin dillancin labaran Xinhua ya ce, ruwa ya mamaye wasu kauyuka yayin da itatuwa suka fadi lokacin da guguwar mai saurin kilomita 125 a kowacce sa’a, ta ratsa kan Yancheng.
Yanzu haka an ruwaito cewar mutane kusan 200 na can dauke da raunuka daban daban.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu