Mutane 500 sun mutu cikin mako guda a Syria
Kungiyar da ke sa ido kan hakkin dan Adam a Syria ta ce, fiye da ‘yan tawaye da dakarun gwamnatin kasar 500 ne suka rasa rayukansu a cikin mako guda da aka shafe ana gwabza yaki da nufin karbe birnin Aleppo daga hannun mayakan jihadi.
Wallafawa ranar:
Shugaban kungiyar Rami Abdel Rahman ya bayyna cewa, akalla fafaren hula 130 ne suma suka mutu sakamakon farmakin da ‘yan tawayen suka kaddamar a yankunan da dakarun gwamnati ke rike da su.
A bangare guda, ‘yan tawayen na Syria sun ce, sun wargaza kawanyar makwanni uku da dakarun gwamnatin suka yi musu a birnin na Aleppo, lamarin da ya dagule ayyukan dakarun da ke samun goyon bayan Rasha.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu