Asiya
An kame mayakan ISIS a Malaysia
Jami'an tsaro kasar Malaysia sun kame mutane 9 da ake zargin ‘yan kungiyar ISIS ne.
Wallafawa ranar:
Talla
Sati biyu da suka gabata ne hukumar ‘yan sandan Malaysia suka kaddamar da sumamen zakulo ‘ya’yan kungiyar ISIS a kasar.
Sifeto Janar din ‘yan sandan kasar Khalid Abubakar ya ce daga cikin wadanda aka kama akwai mutum biyu da suka kai harin gurneti a wata mashaya a Kuala Lumpur a watan Yunin da ya gabata.
Bayan kai harin a mashayar, wani jagoran ISIS a Syria ya dauki alhakin shirya kai harin, wanda ya zama na farko da mayakan suka kai a kasar Malaysia.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu