Isa ga babban shafi
Afghanistan

Afghanistan ta cimma yarjejeniya da 'yan ta'adda

Gwamnatin Afghanistan ta sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya da kungiyar mayakan da ke karkahsin Gulbuddin Kekmatyr, abin da ake ganin zai ba shi damar sake dawowa fagen siyasar kasar.

Gulbuddin Hekmatyar da ya kaddamar da hare-haren ta'addanci  a Afghanistan
Gulbuddin Hekmatyar da ya kaddamar da hare-haren ta'addanci a Afghanistan DR
Talla

Tsohon Firaministan kasar Gulbuddin Hekmatyarne ya taka muhimmiyar rawa a lokacin yaki da mamayar Soviet a shekarar 1980.

Bayan wannan yakin ne, arangama tsakanin kungiyarsa da ta Taliban ta tilasta masa tserewa daga kasar, in da shi da mayakansa suka ci gaba da kai munannan hare-hare a cikin kasar, yayin da Amurka ta sanya sunansa a jerin wadanda take nema ruwa a jallo.

Sai dai bayan cimma wannan yarjejeniyar zaman lafiyar,  gwamnatin Afghanistan ta amince ta yafe wa Gulbuddin duk laifukan da ya aikata a baya na kaddamar da munannan hare-haren ta’addancin da ya yi sanadiyar rayukan daruruwan mutane.

Tun bayan zaben shugaba Ashraf Ghani, al’ummar kasar ke sa ran ganin ya samar da tsaro ta hanyar tattaunawa da kungiyoyi irinsu Hezb-e Islami masu tayar da kayar baya.

Duk da cimma wannan matsaya dai, masharhanta  na ci gaba da bayyana shakku dangane da tasirin wannan yarjejeniya wajen samar da tsaro ga jama'a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.