Isa ga babban shafi
Isra'ila

Isra’ila na shirin takaita kiran Sallah

Firaministan Isra’ila Benyamin Netanyahu ya goyi bayan wani kudirin doka da ke magana akan takaita kiran Sallah a Masallatan Kudus da na sassan kasar, matakin da kungiyoyin kare hakkin bil’adama suka danganta a matsayin barazana ga ‘yancin gudanar da addini.

Masallacin birnin Kudus
Masallacin birnin Kudus REUTERS/Eliana Aponte/File Photo
Talla

Netanyahu ya amince da kudirin dokar ne a lokacin da ya ke ganawa da ministocinsa.

Kudirin yanzu na shirin tsallake karatu na uku a Majalisa kafin ya zama doka, wanda ya kunshi haramta yin amfani da lasifika a lokacin kiran sallah.

Kafofin yada labaran Isra’ila sun ruwaito Netanyahu na cewa ya goyi bayan matakin ne saboda yadda kiran sallan ke damun ‘yan kasa.

Larabawa dai sun kunshi kashi 17.5 na al’ummar Isra’ila yawancinsu Falasdinawa musulmi a gabashin birnin Kudus da ke zargin Yahudawa na danne su.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.