Isa ga babban shafi
Vietnam-China

Kasashen ASEAN na taro kan tsaro a Manila

A yayin da kasashen kasashen yankin yamma maso gabashin nahiyar Asiya, ASEAN suka fara taro a birnin Manila na Philippines kan sha'anin tsaro, kasar Vietnam ta bukaci takwarorinta da su dauki tsattsauran mataki kan yadda China ke ci gaba da mamaye tekun yammacin Sin.

Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Yamma maso gabashin Asiya a birnin Manila na Philippines
Ministocin Harkokin Wajen Kasashen Yamma maso gabashin Asiya a birnin Manila na Philippines REUTERS/Mohd Rasfan
Talla

Vietnam ta bayyana haka ne a yayin da Ministocin Harkokin Wajen kasashen suka fara tattaunawa kan sha’anin tsaro da kuma shirin mallakar makami mai linzami na Korea Ta Arewa.

A gobe Lahadi ne ake saran manyan jami’an diflomasiyar China da Amurka da Rasha da Koriya ta Arewa za su halarci taron.

Taron na zuwa ne a yayin da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ke shirin kada kuri’a kan kudirin da Amurka ta gabatar don tsananta takunkumi kan Korea ta Arewa bisa gwaje-gwajenta na makami linzami.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.