Saudiya
'Mayakan Huthi sun harba roka Saudiya'
Kasar Saudi Arabia ta ce ta kakkabo wani makamin roka da ‘Yan Tawayen Huthi da ke Yemen suka harba zuwa Riyadh.
Wallafawa ranar:
Talla
Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ce an harba makamin ne da misalin karfe 10.50 a dai-dai lokacin da ake shirin gabatar da kasafin kasar a fadar Yamamah.
Saudi Arabia ta bayyana cewar makamin na Huthi kirar kasar Iran ne.
Wannan shine karo na 2 da ‘yan tawayen ke harba irin wannan makami a cikin watanni biyu. A shekara ta 2014 mayakan Huthi suka karbe ikon birnin Yemen.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu