Isa ga babban shafi
Myanmar

Dubban 'yan Myanmar sun cigaba da zanga-zangar adawa da sojoji

Dubban ‘yan Myanmar a ranar Lahadi sun cigaba da zanga-zangar adawa da juyin mulkin kifar da gwamnatin Aung San Su Kyii da sojoji suka yi a kasar.

Dubban masu zanga-zangar adawa da juyin mulki a Yangon babban birnin kasar Myanmar.  7/2/2021.
Dubban masu zanga-zangar adawa da juyin mulki a Yangon babban birnin kasar Myanmar. 7/2/2021. AFP
Talla

Zanga-zangar na cigaba da yin karfi ne duk da matakin katse layukan Intanet dana wayoyin hannu da gwamnatin sojin kasar ta Myanmar ta dauka, wanda rahotanni suka ce ta sassauta shi.

Bayanai sun ce akalla mutane dubu 100 suka fita zanga-zangar adawa da juyin mulkin sojin na Myanmar a Yangon babban birnin kasar, yayinda wasu dubban suka fantsama kan titunan sauran birane.

Ranar Litinin da ta gabata, malamai da dalibai akalla 200 suka kaddamar da zanga-zangar kin jinin sojojin Myanmar a babbar jami’ar kasar ta Dagon.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.