Dan sanda ya mutu a harin da aka kai Majalisar Dinkin Duniya a Afghanistan
Wani dan sandan Afghanistan ya mutu yayin wani hari da aka kai harabar ginin majalisar dinkin duniya a birnn Herat, a yayin da ake ci gaba da baiwa hammata iska tsakanin mayakan Taliban da dakarun gwamnati a wajen birnin da ke yammacin kasar.
Wallafawa ranar:
Rikici ya ta’azzara a kasar ne a farkon watan Mayu, lokacin da kungiyar Taliban ta kaddamar da munanan hare hare a sakamakon karkare janyewar sojojin kasashen waje dake karkashin jagorancin Amukra daga kasar.
Mayakan Taliban din sun karbe iko da gundumomi da dama a kasar, ciki har da lardin Herat, inda suka kuma kwace iyakoki biyu da suka hade Iran da Turkmenistan.
A jiya Juma’a, ‘yan Taliban din sun gwabza fada da dakarun gwamnati a wajen birnin na Herat, lamarin da ya tilasta wa iyalai da dama arcewa daga gidajensu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu