Isa ga babban shafi

Tarwatsewar bam ta jefa miliyoyin 'yan Afghanistan cikin duhu

Hukmomin Afghanistan sun ce miliyoyin mutane  daga larduna 11 ne ke fuskantar rashin wutar lantarki a kasar a Asabar din nan, bayan aukuwar fashe fashe a wasu manyan turakun wutar lantarki a yammacin babban birnin kasar Kabul.

Mayaka masu iikirarin jihadi su na yawan kai hare hare sassan babban birnin Afghanistan, Kabul.
Mayaka masu iikirarin jihadi su na yawan kai hare hare sassan babban birnin Afghanistan, Kabul. Reuters
Talla

Wannan rashin wutar lantarki na zuwa ne a daidai lokacin da ake daf da bukuwar salla karama ta Eid al- Fitir, wadda ke alamta karshen azumin watan Ramadan.

A daren Juma’a ne wasu suka dasa bama bamai a turakun lantarki 2, kuma suka tarwatse, lamarin da ya haddasa rashin wutar a babban birnin kasar da makwaftanta.

A yayin da hukumomi ke kokarin gudanar da gyara na wucin gadi do a samu wuta a daren Asabar dina nan, ‘yan sanda sun ce sun kama wasu mutane 2 da ake zargi da dasa bama baman.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.