Isa ga babban shafi

Girgizar kasa ta kashe karin mutane biyar a Afghanistan

Wani babban jami’in gwamnatin Afghanistan ya ce, kasar ba ta da wadatattun magungunan kulawa da wadanda suka jikkata sakamakon girgizar kasar da ta yi sanadin mutuwar mutane sama da 1,000 a makon da ya gabata.

Wani dattijo a gefen gidansa da girgizar kasa ta rusa a Afghanistan.
Wani dattijo a gefen gidansa da girgizar kasa ta rusa a Afghanistan. AP
Talla

Kalaman jami’in sun zo ne a yayin da, wata karamar girgizar kasar da ta afku a ranar Juma'a ta kashe karin mutane biyar.

A halin da ake ciki, mahukuntan Afghanistan sun kawo karshen laluben mutanen da suke yi a tsaunuka masu nisa dake kudu maso gabashin kasar domin neman wadanda suka tsira daga girgizar kasa mai karfin maki 6.1 da ta afku a safiyar ranar Laraba kusa da kan iyakar Pakistan.

Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da mutuwar mutane 1,036, tare da jikkatar kimanin wasu 2000 a girgizar kasar ta ranar Laraba, kamar yadda Mohammad Nassim Haqqani, kakakin ma'aikatar kula da ayyukan jinkai ta Afghanistan, ya tabbatar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.