Isa ga babban shafi

An kwashe mutane fiye da dubu 100 saboda ambaliyar ruwa a Pakistan

Hukumar Bada Agajin Gaggawa ta kasar Pakistan ta sanar da cewa, kimanin mutane 100,000 ne aka kwashe daga kauyukan da ambaliyar ruwa ta mamaye a lardin Punjab na kasar.

Yadda ambaliyar ruwa ta mamaye wani yanki a Pakistan.
Yadda ambaliyar ruwa ta mamaye wani yanki a Pakistan. REUTERS/Fayaz Aziz
Talla

Kauyuka da dama da dubban kadada na gonakin noma a lardin tsakiyar kasar sun kasance a cikin ruwa lokacin da kogin Sutlej ya balle a ranar Lahadi.

Shugaban gwamnatin Punjab, Mohsin Naqvi, ya ce ruwan sama ya sanya hukumomi a India sakin ruwa mai yawa a cikin kogin Sutlej, wanda ya haifar da ambaliya a gefen iyakar Pakistan.

" Ruwan ya zo ne kwanaki biyu da suka gabata kuma dukkanin gidajenmu sun nutse," in ji Nagvi wani mazaunin yakin da ke shaida wa Kamfanin Dillancin Labarai na  AFP abin da ya faru.

Kasar da ke Kudancin Asiya, na samun kashi 70-80 cikin 100 na ruwan sama a tsakanin watan Yuni da Satumban kowace shekara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.