Kasar Guinee maganar tsaro kan zaben kasar
Jami’an tsaron a kasar Guinee Conakry, sun bankado wani shirin kawo tashin hankali da wasu ke kokarin yi, a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben shugaban kasa zagaye na biyu. Praminista kasar Jean-Marie Dore ,ya ce an cafke wadanda ake zargin da neman kawo hargitsi ga shirin da kasar ke yi na madda mulki ga hunnun farar hula.Ya ce ,mutanen sun nemi kayen sarki irin na jami’an tsaro da nufin yin shigar burtu. Babban habsan sojan kasar Kanal Nouhou Thiam ya tabbatar da labarin.Shugaban kasar ta Guinee Conakry Janar Sekouba Konate ya yi alkawarin maida kasar bisa tafarkin demokaradiya, inda ake shirin gudanar da zaben shugaban kasa zagaye na biyu.
Wallafawa ranar: