Turkiyya - Israela
Gwamnatin Kasar Turkiya ta yi Tir da Rohoton Isra'ila
Prime Ministan kasar Turkiya, Recep Tayyip Erdogan, ya yi Allah wadai da binciken da Isra’ila ta gudanar kan harin da dakarunta suka kai kan tawagar dake dauke da kayan agaji zuwa Yankin Zirin Gaza na Palestinawa, wanda rahotan ya ce bai sabawa dokokin kasashen duniya ba.Erdogan ya ce, ya za’a ce rahotan da Isra'ila ta bayar, wanda ya binciki aiyukan jami’anta, zai fadi gaskiya akan ta.Prime Ministan ya ce zasu ci gaba da bin lamarin
Wallafawa ranar: