Isa ga babban shafi
Iran-Amurka-EU

Iran ta bude hanyar tattaunawa da kasashen Yammaci

Shugaban kasar Iran Mahmoud Ahmadinejad yace gwamnatin shi, a shirye take domin hawa teburin sasantawa da manyan kasashen duniya, game da shirin Iran na kera makaman nukiliya bayan karfafawa kasar Takunkumi.

Shugaban kasar Iran Mahmoud Ahmadinejad
Shugaban kasar Iran Mahmoud Ahmadinejad
Talla

Gwamnatin Musuluncin Iran dai ta musanta zargin da kasashen ke yi game da shirinta na Nukiliya.

Kafafen yada labarun kasar, sun rawaito Shugaba Ahmedinejad na mayar da maratani kan kiran da hukumomin birnin Washington ke yi don sasantawa, inda yace babu bin da zai hana shi tattaunawa da kasashen yamma.

Taron farko da aka gudanar a bara domin warware rikicin Iran tsakanin kasashen Birtaniya da China da Faransa da Jamus da Rasha da Amurka an tashi ne baran-baram ba tare da sasantawa ba.

Shugabar harakokin kasashen wajen Kungiyar Tarayyar Turai, Catherine Ashton tace sun aika wa Iran da sako domin neman zama teburin sasantawa.

Sai dai har yanzu kasashen suna jiran amsar sakon da Ashton ta aika wa Iran a Watan Octoban bara.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.