Isa ga babban shafi
Syria-Amurka-Birtaniya

Obama da Cameron sun yi Allah waddai da rikicin Syria

Shugaban kasar Amurka Barack Obama yace luguden wutar da dakarun kasar Syria ke yi a birnin Homs abun bakin ciki ne, inda Fira Ministan kasar Birtaniya David Cameron ya zargi Gwamnati karkashin shugaba Bashar al-Assad da yunkurin hallaka mutanen kasar.  

Wani yankin birnin Homs da ake wa luguden wuta ya tirnike da hayaki.
Wani yankin birnin Homs da ake wa luguden wuta ya tirnike da hayaki. Reuters
Talla

Mista Cameron, wanda ke Magana a birnin Stockholm na kasar Sweden, ya nemi kawo sauyi ga gwamnatin kasar, inda yace kasashen duniya ba zasu amince da abin da ake gani a akwatunan talibijin ba, inda ake wa masu zanga-zanga dirar mikiya a birnin Homs.

A cewar shugaban, hotunan sun nuna yadda gwamnatin shugaba Al-Assad ke ci gaba da luguden wuta domin murkushe al’ummar kasar.

A jiya Alhamis ‘Yan rajin kare hakkin Bil’adama sun ce mutane 110 ne aka kashe a birnin Homs inda dakarun gwamnati ke ci gaba da kokarin murkushe masu zanga-zanga.

Kasar Jamus kuma ta yi maraba da yiyuwar sake kai ziyarar kungiyar kasashen larabawa a cikin kasar.

Majalisar Dinkin Duniya tace sama da mutane 5,000 ne suka mutu tun fara zanga-zangar adawa da gwamnatin shugaba Bashar Al Assad.

A makon jiya ne Kasar Amurka da Birtaniya suka janye jakadunsu daga kasar Syria saboda fargabar tsaro da rashin amincewa da yadda ake ci gaba da murkushe masu zanga-zangar adawa da gwamnatin Bashar al Assad.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.