Lebanon za ta fara karbar makamai daga Faransa
Faransa ta ce kasar Lebanon za ta fara karbar makaman da Saudiya ta biya daga hannunta a watan Afrilu mai zuwa don yaki da mayakan kasar da ke da’awar Jihadi. Ministan harkokin wajen Faransa Laurent Fabius ne ya tabbatar da haka a lokacin da ya ke ganawa da Firaminsitan Lebanon Tammam Salam a birnin Munich na Jamus.
Wallafawa ranar:
Saudiya ce dai ta yi alkawalin biyan kudin makaman daga Faransa da suka hada da makaman Atilare da kuramen jirage yaki da masu liken asiri da kuma motocin yaki masu sulke.
Shugabannin kasashen biyu sun yi kira ga kungiyar Tarayyar Turai ta kawo wa Lebenon dauki wacce ke hidima da miliyoyan ‘yan gudun hijirar Syria.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu