Isa ga babban shafi
Turkiya

Mutane 10 sun mutu a mummunan harin da aka kai a Istanbul

Akalla mutane 10 suka mutu yawancinsu Jamusawa a wani mummunan harin da wani dan kunar bakin wake da aka ce Dan Syria ne ya kai a birnin Istanbul na Turkiya.

Jamusawa 9 suka mutu a harin Istanbul
Jamusawa 9 suka mutu a harin Istanbul © Reuters
Talla

An kai harin ne a yankin Sultanahmet kusa da wani babban masallaci.

Akalla Jamusawa 9 ‘yan yawon bude ido aka kashe daga cikin mutane 10.

Sannan kimanin 15 suka jikkata a harin, yayin da rahotanni suka ce biyu daga cikinsu na cikin mawuyacin hali.

Yankin da aka kai harin wuri ne na tarihi da baki ‘yan kasashen waje ke kai ziyarar yawon bude ido.

Shugaban Turkiya Raceep Tayyib Erdogan, ya yi tir da harin, a jawabin da ya yi wa ‘yan kasar.

An danganta harin cikin munanan hare haren da aka taba ka iwa a Turkiya bayan harin watan Oktoba da aka kai a Ankara inda aka kashe mutane 103.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.