Libya
Sojan Libya sun kubutar da 'yan kasashen waje 13 daga hannun kungiyar IS
Sojan Libya sun kubutar da wasu ‘yan kasashen waje akalla 13 daga hannun mayakan kungiyar IS masu ikirarin jihadi da kafin tsiya, wadanda aka yi garkuwa da su a yankin garin Sirte.
Wallafawa ranar:
Talla
Wata sanarwa daga Sojan Libyan na cewa cikin wadan da aka kubutar akwai dan kasar Turkiyya daya da dan kasar Masar daya da kuma mata 11 ‘yan kasar Eritrea.
Sojan Gwamnatin Libya na fafatawa ne da ‘yan kungiyar IS a maboyar su ta karshe a Sirte domin kawo karshen su a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu